Da Aka Fi Sani Da Malamai Masana Allah Da Addininsa Imam Mahadi (a.s) Ya Ba Su Damar Tafiyarwa Ko Kuwa Wani Abu Ne Ya Ba Su Dama Ban Da Sauran Abubuwa?! A nan ne aka tayar da jijiyoyin wuya kan mas'ala mai girma ta jagoranci; yayin da wasu daga malamai suka tafi a kan cewa; Imam Mahadi (a.s) a matsayinsa na jagoran al'umma da ya boyu daga ganewarta ta yadda suna iya ganinsa amma ba sa iya gane shi, ya bar wa malami mas'alar fatawa, da khumusi, da ganin wata ne, don haka duk wani mutum dole ne ya bi malami a kan wadannan abubuwan. Amma batun jagorancin al'umma wanda aka fi sani da siyasar musulunci ko kusa ba na malami ba ne, kuma bai samu wannan damar daga Imami (a.s) ba. Shin Wani Mutum Wanda Ba Ma'asumi Ba Ne Zai Iya Warware Matsalar Al'umma? Tambaya kan wannan lamarin ta zo ne sakamakon cewa muna iya ganin yadda dan Adam ya kasa warware matsalar rayuwarsa yayin da tururuwa da gara tun da Allah ya halicce su sun warware matsalarsu ta tattalin arziki da jagoranci da zamantakewar al'umma! A nan muna iya tambaya cewa shin wadannan kwari sun fi daraja wurin Allah fiye da dan Adam ne ko kuwa? Wa Ya Kamata Ya Kasance Jagoran Mutane? Shi dai lamarin siyasar al'umma wato; jagorancinta wani abu ne da ya kamata ya kasance karkashin dabi'u na gari da 'yan'uwantaka, da kaunar juna, da mutunta juna, da son al'umma, da jin daukar nauyin yi musu hidima, da ganin kimar dan Adam,wannan kuwa lamari ne da yake cikin dukkan wani loko na rayuwar al'umma da ya hada da zamantakewa, da tattalin arziki, da dukkan janibobin rayuwa, Imam Ali (a.s) yana cewa: Mutane ‘yanuwa ne, duk wanda ‘yanuwantakarsa ba ta kasance saboda Allah ba to gabace, wannan kuwa saboda fadin Allah madaukaki: “Ma’abota a wannan rana makiyan juna ne sai dai masu tsoron Allah”. Surar Zuhuruf: 67. Siyasar Musulunci Ko Musuluncin Siyasa?! Siyasar musulunci: Al'amari ne da ya shafi jagorancin jama'ar musulma kamar yadda yake bisa dokokin shari'a. Amma musuluncin siyasa abu ne maras kyau, domin shi ne amfani da wata manufa domin samun cimma wani hadafi da guri.
Ma'anar farko wato siyasar musulunci tana da kyau domin amfani ne da siyasa domin yin hidima ga addini, amma ma'ana biyu ta munana matuka domin tana nufin a yi amfani da musulunci ne domin cimma wani buri ko hadafi na siyasa, wannan lamari matuka ya munana kuma mun ga misalansa a siyasar duniya a kasashe daban-daban. Kuma da ma'ana ta biyu ne wasu suka yi raddi ga wani shehi kan sukan da ya yi wa babban marja'in nan Ayatul-Lahi Sistani (H), suka nuna cewa sukan da ya yi wa mar'ja'in kan wasu mas'aloli yana iya komawa zuwa ga cewa; shi mai sukan ya riki musuluncin siyasa ne ba siyasar musulunci ba!.
Amma da kake cewa: Amma da kake cewa: ((3) Matsayin Annabi Muhd SAW a Addinin Shi'a, Wannan Annabi da suke karyar so da yadda suke yaudarar wawaye da son yayan gidansa, zaka ga abinda suke fada a kansa. Majlisi Zinkidi yana fada a littafinsa Biharur Anwar shafi na 43 cewa "Annabi `SAW' baya iya bacci har sai ya sunbaci Fatima a tsakanin nonuwanta" to kaga wannan babbar alama ce da ta nuna kuna kaunar Annabi yan Shi'a, sai yasa Jaza'iri ya fada a Anwarunnu'umaniyyah Mujalladi na daya shafi na 17 "Aliyu yafi Annabi Muhd Jarumta koda yace shi Annabi Muhd dama can ba jarumi bane tun asali" to don haka karku ga na kafe akan ra'ayi na na cewa Shi'a ba Musulunci bace addini ce mai zaman kansa ku zarje ni ina da hujja)). Da Sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai A yau na bude wannan shafin "nana_fatima" sai na ga wannan abin mamaki na hujumi kan masoya Ahlul Baiti (a.s) sai na ga ya kamata in tofa albarkacin bakina; musamman duba zuwa ga cewa; wasu miyagun akidu sun shigo da suke nuni da raini ga Ahlul Baiti (a.s) da matsayinsu. Mai magana ya yi wa rubutunsa taken: ((HATTARA DAI MUSULMI 2!!)) sannan sai ya ci gaba da cewa: ((A rubutu na da ya gabata ya tada hankalin da yawa daga mabiya Addinin Shi'a na wannan majalisa kai harma da yan'uwa Musulmi wayanda basu gama gano sharrin Addinin Shi'a ba har suke daukarsa wani bangare ne daga Addinin Musulunci kamar yadda yahudawa da kiristoci suke rayawa cewa su addinaine haka shian'ci yake a matsayin addini mai zaman kansa)). Fatawar mai girma Shaikhul Azhar kan halalcin aiki da Mazhbar Shi'a Ithna Ashariyya: An tambaye shi cewa: "Wasu mutane suna ganin wajibi ne kan musulmi ya yi taklidi (koyi) da mazhabobin nan guda hudu sanannu, kuma babu mazhabar Shi'a Imamiyya ko Shi'a Zaidiyya a cikinsu, domin aikinsa na ibada da mu'amala ya zama ingantacce, karbabbe. Shin Malam yana muwafaka da wannan ra'ayi, misali yana hana aiki da mazhabar Shi'a Imamiyya, ga misali?"
Sai Mai girma ya amsa da cewa:
1. Lalle addinin Musulunci ba ya wajabtawa wani daga mabiyansa da ya bi wata mazhaba kebabbiya. Kai kowani musulmi yana da hakkin, tun daga farko, na ya bi kowace mazhaba wacce aka nakalto ta nakaltowa sahihiya wacce aka rubuta hukumce-hukumcenta cikin littattafanta kebantattu. Kuma duk wanda yake bin wata mazhaba daga wadannan mazhabobi yana da damar ya koma wata mazhabar, kowace ce kuwa. Kuma ba shi da laifi kan kome daga wannan.
Musulmi Al'umma Ce Guda "Kuma ku yi riko da igiyar Allah gaba daya, kuma kada ku rarraba. Kuma ku tuna ni'imar Allah a kanku, a lokacin da kuka kasance makiya, sai Ya sanya soyayya a tsakanin zukatanku, saboda haka kuka wayi gari, da ni'imarSa, 'yan'uwa. Kuma kun kasance a kan gabar rami na wuta, sai Ya tsamar da ku daga gare ta. Kamar wannan ne Allah Yake bayyana muku ayoyinsa, tsammaninku, za ku shiryu # Kuma wata jama'a daga cikinku, su kasance suna kira zuwa ga alheri, kuma suna umurni da alheri, kuma su na hani daga abin da ake ki. Kuma wadannan su ne masu cin nasara # Kuma kada ku kasance kamar wadanda suka rarrabu, kuma suka saba wa juna, bayan hujjoji bayyanannu sun je musu, kuma wadannan suna da azaba mai girma". (Surar Aali Imrana, 3: 103-105)
"Saboda haka, ka tsayar da fuskarka ga addini, kana mai karkata zuwa ga gaskiya, halittar Allah da Ya halitta mutane a kanta. Babu musanyawa ga halittar Allah, wannan shi ne addini madaidaici, kuma amma mafi yawan mutane ba su sani ba # Kuma masu mai da al'amari gare Shi kuma ku bi Shi da takawa, kuma ku tsayar da salla, kuma kada ku kasance daga mushirikai # Watau wadanda suka rarrabe addininsu, kuma suka kasance kungiya-kungiya, kowace kungiya tana mai farin ciki da abin da ke a gare ta kawai. (Surar Rum, 30: 30-32)
"Kuma abin da kuka saba wa juna a cikinsa, ko mene ne, to hukumcinsa (a mayar da shi) zuwa ga Allah. Wancan Shi ne Allah Ubangijina, a gare Shi na dogara, kuma zuwa gare Shi nake mayar da al'amarina. (Surar Shura, 42: 10)
Dubi Cikin Mazhabobin Fikihu A zamanin Manzon Allah (s.a.w.a.) musulmi suna samun hukumce-hukumce da dokoki masu tsara al'amurransu na zamantakewa da ibada, kamar su salla, rabon gado, zaman iyali, kasuwanci, jihadi, aikin hajji da abin da ya shafi kasa da filaye da shari'u da sauransu ne kai tsaye daga Annabi (s.a.w.a), domin shi ne mai isar da sako, mai kira zuwa ga shiriya ta hanyar wahayi.
Bayan da ya koma ga Ubangijinsa Mahalicci, al'ummar musulmi sun koma ga Littafin Allah da Sunnar Ma'aiki (s.a.w.a.), suna daukar dokoki da sanin ra'ayin shari'a kan dukkan abubuwan da suka shafe su ta hanyar sahabbai da Ahlulbaiti (a.s), wadanda suka kiyaye Sunna da kuma Littafin Allah. Daga nan al'ummar musulmi ta sami ci gaba cikin salon rayuwa, saboda faruwar sabbin abubuwa cikin rayuwar mutane. Babu shakka wadannan sabbin abubuwa suna bukatar hukumcin Musulunci da sanin dokokin shari'a domin daidaitasu. Wannan fadada-wa cikin shari'a ya fara samuwa kusan a karshen karnin farko a zamanin Imam Muhammad Bakir (a.s.), wanda shi ne malamin Madina, kuma mokamar dukkan malaman zamaninsa. Malaman tarihi da na fikihu sun ruwaito cewa saboda hakan ne ma ake kiransa da Al-Bakir, domin fadadawarsa wajen ilmomi da yada su. A zamanin dansa Imam Ja'afar Sadik (a.s.) ne fannonin ilmi da fikihu da shari'a suka yi fure, yayin da shugabannin Tafarkin Ahlulbaiti (a.s) Kan Ayyukan Siyasa Duk wanda ya bibiyo salon siyasar Ahlulbaiti (a.s) da gwagwarmayarsu ta bayyane da ta boye a tsawon karno-ni biyu da rabi zai iya gano cewa aikin da suka yi na siyasa yana bisa ginshikai kamar haka:
(1). Tarbiyyantar da al'umma kan kin zalunci da tabbatar da manufar adalci da bayyana fikirar imamanci da siyasa da fayyace rukunan hukumci da shugabanci cikin addinin Musulunci. Sun yi haka ne domin karfafa fahimtar siyasa ga al'umma da karfafa kulawarta da kiyayyarta ga azzalumai, da farkar da ita daga barci. Wanda ya yi bitar abin da Ahlulbaiti (a.s) suka ruwaito suka watsa daga Manzon Allah (s.a.w.a.) dangane da wannan al'amari, zai gane muhimmancin wannan mataki wajen farfado da ruhin siyasa da kiyayewa ta Musulunci. A nan za mu ambaci wasu daga cikin ruwayoyin da suke magana dangane da shugabanci da kuma nauyin da suka hau kan shugaba musulmi, da kuma kyamar da Musulun-ci yake wa zalunci da kuma kira zuwa ga adalci, don mu fahimci fikira da tunanin Ahlulbaiti (a.s) wajen fada da zalunci da kuma kwadaitar da al'umma zuwa ga canji da kuma motsi na siyasa.
An ruwaito daga Imam Muhammad Bakir (a.s.) cewa wani dattijo daga kabilar Nakh'a ya ce:
|
|